Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ada Abubakar na 3 ya yi kira ga gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da ta sassauta batundokar nan da ta hana shigo da shinkafa da motoci ta kan iyayokin kasa ta Nijeriya sai ta ruwa
Sarkin ya yi wannan kiran ne a jiya a lokacin da mukaddashin shugaban Nijeriya Farfesa Yemi Osinbajo ya kai masa ziyara a fadarsa da ke Sokoto
Sarkin Musulmi ya ci gaba da bayyana cewa wadannan manufofi basu yi daidai da yanayin da kasar ke ciki ba a halin yanzu na tabarbarewar tattalin arziki
“Za mu ci gaba da zama muryar marasa murya (talaka), kuma a wannan nukuda, ba za mu gajiya da kiran gwamnati da ta yi dubu tare da sassauta wasu manufofi nata ba ta yadda talaka zai samu sa’ida” inji Sarkin Musulmi ya ce
“‘Yan Nijeriya na cikin mawuyacin hali, a saboda haka ya zama wajibi gwamnati ta sassauta manufofinta ta yadda al’umma za ta samu sauki. Wannan ita ce hanyar da za ta samar da fahimtar juna tsakanin gwamnati da jama’a”
“Muna jaddadawa gwamnati tabbacin hadin kanmu da goyon bayanmu a kowane lokaci, amma wadannan manufofi biyu sam sun zo a lokacin da bai dace ba.” A cewar Sarkin Musulmin Sa’ad Abubukar na 3
Sarkin ya yi wannan kiran ne a jiya a lokacin da mukaddashin shugaban Nijeriya Farfesa Yemi Osinbajo ya kai masa ziyara a fadarsa da ke Sokoto
Sarkin Musulmi ya ci gaba da bayyana cewa wadannan manufofi basu yi daidai da yanayin da kasar ke ciki ba a halin yanzu na tabarbarewar tattalin arziki
“Za mu ci gaba da zama muryar marasa murya (talaka), kuma a wannan nukuda, ba za mu gajiya da kiran gwamnati da ta yi dubu tare da sassauta wasu manufofi nata ba ta yadda talaka zai samu sa’ida” inji Sarkin Musulmi ya ce
“‘Yan Nijeriya na cikin mawuyacin hali, a saboda haka ya zama wajibi gwamnati ta sassauta manufofinta ta yadda al’umma za ta samu sauki. Wannan ita ce hanyar da za ta samar da fahimtar juna tsakanin gwamnati da jama’a”
“Muna jaddadawa gwamnati tabbacin hadin kanmu da goyon bayanmu a kowane lokaci, amma wadannan manufofi biyu sam sun zo a lokacin da bai dace ba.” A cewar Sarkin Musulmin Sa’ad Abubukar na 3
Sarkin Musulmi Ya Yi Kira Ga Buhari Da Ya Janye Dokar Hana Shigo Da Shinkafa Da Mota
Reviewed by Unknown
on
March 09, 2017
Rating:
No comments: