Kungiyar Dattawan Yankin Neja
Delta a kudancin Najeriya ta ba
Gwamnatin kasar wa’adin
zuwa ranar 1 ga watan
Nuwamba ta biya bukatunta ko
kuma ta fice daga tattaunawar
samun zaman lafiya da suke yi
tsakaninsu.
Tawagar shugabannin a
karkashin Chief Edwin Clark ta
ce sun ba Gwamnati bukatun
16 cikinsu har da yaki da talauci
a Yankin domin kawo karshen
hare haren da ake kai kan
bututun mai, amma gwamnati
ta kasa aiwatarwa.
A watan Nuwamban bara ne
shugabannin yankin na Neja
Delta suka mikawa shugaba
Buhari bukatunsu 16, matakin
da ya takaita hare haren
tsagerun yankin akan kadarorin
gwamnati.
Bukatun sun hada da dawo da
dawo da manyan ofisoshin
kamfanonin mai zuwa kudancin
kasar da kara ware kudaden
tallafi domin ci gaban yankin.
Mista Clarke ya ce za su fice
tattaunawar idan har
gwamnati ta gaza cimma
bukatunsu.
Delta a kudancin Najeriya ta ba
Gwamnatin kasar wa’adin
zuwa ranar 1 ga watan
Nuwamba ta biya bukatunta ko
kuma ta fice daga tattaunawar
samun zaman lafiya da suke yi
tsakaninsu.
Tawagar shugabannin a
karkashin Chief Edwin Clark ta
ce sun ba Gwamnati bukatun
16 cikinsu har da yaki da talauci
a Yankin domin kawo karshen
hare haren da ake kai kan
bututun mai, amma gwamnati
ta kasa aiwatarwa.
A watan Nuwamban bara ne
shugabannin yankin na Neja
Delta suka mikawa shugaba
Buhari bukatunsu 16, matakin
da ya takaita hare haren
tsagerun yankin akan kadarorin
gwamnati.
Bukatun sun hada da dawo da
dawo da manyan ofisoshin
kamfanonin mai zuwa kudancin
kasar da kara ware kudaden
tallafi domin ci gaban yankin.
Mista Clarke ya ce za su fice
tattaunawar idan har
gwamnati ta gaza cimma
bukatunsu.
Yan Neja Delta sun ba gwamnatin Najeriya wa’adi
Reviewed by Unknown
on
August 01, 2017
Rating:
No comments: