Duniya Ta Yi Allah Wadai Da Harin Kunan Bakin Waken Da Aka Kai Jihar Bornon Nigeriya


Majalisar Dinkin Duniya ta yi Allah wadai da hare-haren kunan bakin waken da aka kai garin Mandarari da ke jihar Borno a shiyar arewa maso gabashin tarayyar Nigeriya a jiya Talata. Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi tofin Allah tsine tare da yin Allah wadai kan jerin hare-haren kunan bakin wake da wasu mata uku suka kai garin Mandarari da ke karamar Hukumar Konduga a jihar Borno da ke shiyar arewa maso gabashin tarayyar Nigetriya a yammacin jiya Talata, inda jerin hare-haren suka lashe rayukan mutane akalla 30 tare da jikkatan wasu fiye da 80 na daban. Shaidun ganin ido sun bayyana cewa: Mace ta farko ta tarwatsa kanta ce a tsakanin jama'a a cikin kasuwa, inda nan take mutane 28 suka rasa rayukansu, yayin da wasu mata biyu na daban suka tarwatsa kansu a kofar mashigar sansanin 'yan gudun hijira da ke kusa da kasuwar, inda suka jikkata mutane akalla 82. 'Yan kungiyar Boko Haram ne dai suka shahara da kai hare-haren kunan bakin wake a tsakanin jama'a a shiyar arewa maso gabashin Nigeriya.
Duniya Ta Yi Allah Wadai Da Harin Kunan Bakin Waken Da Aka Kai Jihar Bornon Nigeriya Duniya Ta Yi Allah Wadai Da Harin Kunan Bakin Waken Da Aka Kai Jihar Bornon Nigeriya Reviewed by Unknown on August 16, 2017 Rating: 5

No comments:

Powered by Blogger.